Friday, 16 January 2015

YADDA ZAHARADDEEN YA ZAMA SADAUKI MAI DUNIYA II

Ci gaba daga makon jiya
Yadda Zaharaddeen ya zama Sadauki Mai Duniya.

Matan nan su kai nasarar mamaye gidajen sarakan Kwairanga in da a karshe su ka kare musu kallon sirri a ranar wani biki na al'ada da Kwairanga ke gudanarwa duk shekara a ka turo maza mayaka daga Damanga, ' yanmata sukashayar da sarakai giyasu bayan sun sha sun bugu su ka hadu su ka cinyesu da yaki da rana tsaka, su ka karkashe mutane su ka nufi fada wajen Sarki, in da ya nuna jarumtarsa a shafi na 9 ' Maharan Damanga su ka yi ca kan Sarki Haruna, shi kuwa gogan naka ko in kula sai faman kirari ya ke yana cewa "Sai ni dan mutan Kwairanga kadangaren bakin tulu, a kar ka a kar tulu a bar ka ka bata ruwa, ruwan dare dama duniya na kwairanga sai dubu ta taru, ai kuwa nan da nan suka taru a kansa su ka kame Sarki Haruna Kabir su ka tafi da shi garinsu su ka daure, cikin matansa kuwa akwai wata da a ke kira Hassana wacce ta haye doki ta kubuta ta gudu tare da goyon danta Usman, 'yar Wani sarki sadauki jarumin gaske ne a wata kasa da a ke kira Yammaniya. Bayan ta sanar da mahaifinta yadda a ka tarwatsa kasar maigidanta Sarki Haruna, sai ya jajanta lamarin kuma ya dauki aniyar horar da Usmanu don ya daukarwa mahaifinsa fansar abinda a ka yi masa.
Sarki Haruna kuwa ya na daure a can wani kurkukun karkashin kasa a kasar Damanga in da ya shafe shekaru cikin wahala da azabtarwa iri-iri, yayin da kuma Zubaida daya daga cikin matan da a ka tura Kwairanga su ka yaudarar da sarakai ta kamu da ciwon son sa ta dinga zuwa har cikin firsuna ta na taimakonsa tare da shan alwashin sai ta fitar da shi daga halin kuncin da ya ke ciki.
Usman na da shekaru bakwai a ka fara shigar da shi daji a na gogar da shi ilimin yaki tun daga kan fada da mutane har zuwa dabbobi tare da koya masa dabarun fada da takobi da mashi da iya harbi da kwari da baka da sauransu.
Ya na da shekaru goma sha biyu ya kware sosai ya zama sadauki a fagen yaki duk kasar yammawa an sallama masa har su na yi masa kirari a shafi na 12 su na cewa " Usman Mai duniya na Kaura yalli, gwaggon biri makashin maza".
A lokacin ne a ka sanar da Usman labarin mahaifinsa da irin wulakancin da Damangawa su ka yiwa masarautarsa.
Ai kuwa Usman Mai duniya ya shirya tare da abokinsa Sabi'u wanda su ka taso tare dan Kaura yalli wato kawun Usmankenan, su ka nausa daji.
Shi kuwa Sarki Haruna Kabir Zubaida ta kubutar da shi daga gidan kurkukun sun shiga duniya, in da suka yi aure daga bisani wahalar da ya sha a kurkuku ta kwantar da shi ciwo.
Jarumta
Usman kuwa tun shigarsu daji ya ke nuna jarumtarsa in da ya kashe Gada suka cinye a shafi na 23, sannan ya gwabza yaki da wasu 'yan rawar wuta a shafi na 26, ya yi gumurzu da Sarkin fawa a shafi na 27. Sun buga gumurzu da mayakan garin Dawaki a shafi na 32 in da su ka biyo bayansu, maimakon Usman ya gudu sai su ka tsaya suna cafe mashi da kibbau, in da ya ke yi wa kansa kirari, "Kai arna ba ku sanni ba ne? Ni ne Usman Mai duniya, gwaggon biri makashin maza ni ne hadari malfar duniya". Nan ya afka musu ya karkashe su.
Haduwarsu da aljani wanda ya ba Usman takobin kakansa da suka ara su kai yaki a shafi na 33-34.
Usman ya shiga gasa a kasar Zainawa in da ya yi dauki ba dadi da mayaka abokan takara a shafi na 36.
Sannan ya gwabza da sarkin yakin garin Kaura Malle wanda manyan baraden nahiyar ke shakkar arangama da shi saboda rashin tausayinsa, amma Usman bai saurara ba sai da ya fatattaka jikin Kaura Malle ya cinye gasar a shafi na 37-39.
Ya taimakawa Sarkin Zainawa sun yaki mutanen kasar Dawaki in da ya gwabza da manyan mazaje da kauraye a shafi na 55 sannan ya yi gumurzu da Sarkin Dawakin in da ya gwada masa cewa jarumta fa ba a karami take ba kuma ba a babba ta ke ba, a wajen mai zuciya ta ke.
Usman da Sabi'u sun gwabza gumurzun yaki da mayakan kasar Damanga a Kasar Dadin kowa a shafi na 88/90.
Sun sake kutsawa yaki kasar Kwairanga daukar fansa domin bayan ture Sarki Haruna Kabir sai Sarki Sakimu ya dora kaninsa Mantau a gadon sarautar kasar, a shafi na 101/103, su Usman Mai duniya da Sabi'u sun kawar da Sarki Mantau yayin da Sarki Haruna ya koma kan gadon Sarautarsa da Damagawa su ka tsige shi.
Jarumtar kwarai mai nuna bajinta da ban sha'awa ta mayakan hadin gwiwan kasar Dadin kowa da Zainawa da Kwairanga da kuma Kaura Yalli na kasar yammaniya ta yi arangama da rundunar mayakan Kasar Damanga domin daukar fansa a kan Sarki Sakimu wanda ya addabi yankin a shafi na 105/110 wannan gumurzu shi ne ma fi hatsarin gaske da sarakunan su ka yi. Mata ma ayarin gimbiya Sailuba sun buga gumurzu karkashin Batulu in da su ka karkashe mazajen Damanga.
Usman ya yi arangama da Sarki Sakimu in da su ka yi ta dauki ba dadi ga juna har dai Usman ya sassare masa hannuwa biyu tun daga kafada duk da ganin an kassara Sakimu Zakin Hamada mayakansa ba su saduda sun gwada tsabar taurin kai da masifa sai da Usman mai duniya ya shayar da su ruwan kokon mutuwa, jini ya dinga kwarara, hannuwa da kafafuwa iri-iri kawuna kuwa ba adadi sannan 'yan tsirarun Damangawa su ka sallama, a ka ja Sarki Sakimu zuwa kasarsa ta Damanga gaban talakawansa da ya ke yiwa zalunci ya ke kashewa da izza a ka kashe shi, a ka ba talakawa zabi su ka zabo wanda su ke so a ka nada musu.
Soyayya,
Sarki Haruna ya yi soyayya da Zubaida a shafi na11/12, 21/24 wacce soyayya ce mai cike da tausayi tare da nunawa juna kauna In da a karshe su ka yi aure.
Usman mai duniya da Gimbiya Sailuba 'yar sarkin Zainawa a shafi na 40/42, 47/48
Soyayya ce ta sadaukarwa da nuna tarairayar juna.
Sabi'u ya yi soyayya ta hakika da Safara'u 'yar hakimin Dawaki a shafi na 27/29 in da ya yi takara da dan Galadiman garin.
Usman ya yi soyayya da Aisha a kasar Dawaki.
Littafin ya cika burin taurarin na daukar fansa tare da kai su karagar sarauta da kuma auren matayen da su ke so.
Bugu
Babu laifi a bisa bugun littafin da kuma wallafuwarsa a dunkulallen littafi guda daya da kasantuwarsa mai sahihiyar lambar bugu ISBN.
Tsarin shafuka ya tsaru.
Zanen bango ya dakko hoton ainahin gumurzun da ke cikin labarin.
Kura-kurai
An ce komin iyawarka da kallo mai kallon ka ya fi ganinka, duk irin kokarin da a ka yi wajen kiyaye dokoki da ka'idodin rubutu an dan samu hadewar wasu kalmomi da ya dace a rarrabasu a shafi na 4 koina maimakon ko'ina
a shafi na 5 suka maimakon su ka.
Irin wadannan kananan kura- kurai dai a kan same su tsilla-tsilla cikin littafin.

YADDA ZAHARADDEEN YA ZAMA SADAUKI MAI DUNIYA

Daga Sa'adatu Baba Ahmad Leadership Hausa
31/01/2014

Hira da Marubuci Zaharaddeen Ibrahim Kallah tare da Sharhin Littafinsa Sadauki Mai Duniya....
Ya ya sunanka?
Suna na Zaharaddeen Ibrahim Kallah
Kadan daga cikin tarihin ka?
An haife ni a unguwar Fagge da ke Kano, na yi makarantar firamare na a makarantar firamare ta Giginyu wanda daga nan kuma na koma firamare ta Race Course da ke filin sukuwa a Kano. Bayan nan na wuce makarantar sakandire ta Stadium don yin karatuna na gaba da firamare. Da na qare ne sai na je kwalegin share fagen shiga jami’a ta CAS, Kano. Daga nan ne na samu shiga jami’ar Bayero da ke Kano in da na yi digiri na karanci abin da ya shafi ilimin zamantakewar xan adam tare da siyasa (Sociology/Political Science). Na yi hidimar qasa ta a jihar Kwara wanda na koyar a wata sakandire da ke Patigi. Bayan nan na fara aiki da NGO na wani lokaci kafin na koma Jami’ar Bayero da aiki. A Bayero na koma na yi digiri na biyu a vangaren karatun ci gaban duniya wato (Development Studies).
Wacce shekara ka fara rubutu?
Na fara rubutu a shekara ta 1995 bayan na qare sakandire, xan zaman da na yi kafin na cigaba da makaranta na ga ya dace na fara rubutu.
Wacce shekara ka fara wallafa littafi?
Kafin fara buga littafi na rubutu na ya fito ne a littattafai na gamayya na turanci a wajen 2002, littafin Hausa kuma sai a 2006 littafina “Ciki Da Gaskiya” da muka yi qarqashin hukumar A Daidaita Sahu ya fito.
A matsayinka na marubucin Hausa da turanci, wanne rubutune ya fi ma sauki da ba ka sha'awa a cikinsu?
A matsayina na Bahaushe babu rubutun da ya fi mun sauqi kamar rubutu da Hausa, a cikinsa ne na fara rubutu da kuma shi ne na buxi ido. Tun a firamare a lokacin ina Monita na kan karantawa ‘yan ajina Littattafai irinsu “Ilya Xan Mai Qarfi”da “Magana Jari Ce”.
Zuwa yanzu me ka fahimta game da salo da harshe?
Salo na nufin tsari na rubutu da marubuci ya yi amfani da shi wajen isar da saqonsa. Salon da ake amfani da shi ya danganta da marubuci, wani kan yi amfani da salo mai sa karsashi da jan hankali, wani kuma kan yi amfani da salo mai wahalar da mai karatunsa.
Harshe hanya ce ta isar da saqonni, wanda ta qunshi kalmomi da suke bada ma’ana. Marubuci na amfani da harshe don isar da saqonsa ga jama’a wanda ya qunshi tunani da falsafa.
Wadanne marubuta ne gwanayenka a marubutan Hausa?
A vangaren rubutun Hausa ina da gwanaye kamar su Bala Anas Babinlata da Nazir Adam Saleh da Ibrahim Sheme da Bature Gagare da Yusuf M. Adamu
A marubutan turanci fa?
A Turanci akwai Sidney Sheldon da Abubakar Gimba da James Hadley.
Littafinka Sadauki Mai Duniya ya bambamta da littattafan wannan zamanin, menene sirrin?
Littafin Sadauki Mai Duniya labari ne da ya waiwayi shekaru sama da xari biyu baya a lokacin da ake yaqe-yaqe a qasar Hausa. Kafin na fitar da littafin sai da na nazarci salo daban-daban musamman littattafai tsofaffi da suka kawo tarihi da adabi na shekaru aru-aru. Da wannan ne na yi qoqarin fitar da littafin Sadauki Mai Duniya.
Wacce kungiya ka ke ciki?
Ina cikin Qungiyar Marubuta ta Najeriya (ANA) reshen jihar Kano, a halin yanzu ni ne Magatakardarta. Sannan ina cikin wasu qungiyoyi da dama waxanda ba na marubuta ba, waxanda suka haxa da na cigaban alumma.
Sharhin Littafin Sadauki mai duniya....
Sadauki mai Duniya Littafin da ya kere sa'a.
marubuci Zaharaddeen Ibrahim Kalla.
Shekarar bugu-2010
Jigon labari- Jarumta
Yawan shafuka- 150
Bugawa da yadawa- madaba'ar iya ruwa Zaria Road, Kano Nigeria.
ISBN- 987-987-087-880-3
Rabona da karanta wani labari na jarumta wanda har na ke ganin jarumtakar ta kai Sadaukantaka tun wani Fim da na gani na shekaru dari uku na Sarki Liyonaidas na kasar Sparta wanda ya fuskanci barazanar murkushewa idan har k'asarsa ba ta yi mubaya'a ba ga Sarkin Zaksia ba Azskiz wanda azzalumin shugaba ne da babu Sarki mai karfinsa a duk duniya a kuma zamaninsa. Sun yi jayayya da Liyonaidas in da ya gaza zubda Liyonaidas wajen kare martaba da 'yancin k'asarsa. Sun gwabza yaki ga juna amma jarumta ta hana Liyonaidas ya yi hakuri ya janye duk da kuwa Sarki Azskiz ya fi shi karfi tare da jama'a. A karshe dai an kashe Sarki Liyonaidas da dubban masu da kibbau amma wajibi ne a jinjinawa jarumtarsa da gwarzantakarsa.
A lokacin da na ke karatun littafin Sadauki mai duniya na yi ta kamanta jarumtar Usman mai duniya da Sarki Liyonaidas yadda a 'yan shekarunsa na kuruciya ya shiga daji ya kashe Karen ruwa shi ma Usman mai duniya 'yan shekarunsa na kuruciya ya shiga daji ya kashe Goggon biri.
Sadauki Mai Duniya
Wannan littafi ya kunshi labarin wasu masarautu guda biyu masarautar Kwairanga wacce ke karkakashin mulkin sarki Haruna wanda ke gudanar da mulkinsa cikin jarumta da adalci da tausayin talakawa. Yayin da daya masarautar Damanga wacce Sarki Sakimu ya ke gudanar da mulkinta cike da zalunci da izza, ya maida rayukan talakawansa tamkar na fari saboda kisan kai da mugunta, sannan duk wani mikirci tare da kulla salon dabarun yaki ya iya, Sarki Sakimu na da dabi'ar bakin ciki a duk lokacin da ya ji labarin kasar da arzikinta ya kafu ko kasar da ta shahara a fagen yaki ya kan so ya yaketa ta dawo karkashin mulkinsa ko ta wacce hanya ne.
Lokacin da Sarki Sakimu ya ji labarin masarautar Kwairanga ya yi tunani ya ga ba zai iya yakarta ba sai ya shirya makirci ya tura wasu kyawawan mata wadanda kyaunsu ya kai kyau su ka je fada a zuwan 'yan gudun hijirar yaki wanda su ka ce Damangawa sun kashe iyayensu da mazajensu, a taimake su da wurin zama. Sarki Haruna Kabir dai zuciyarsa ba ta kwanta da lamarin ba saboda ya gansu tsaf-tsaf ba wahala ko gajiyar tafiya a tattare da su amma 'yan majalisarsa su ka nuna ba wani abu. Matan nan su kai nasarar mamaye gidajen sarakan Kwairanga in da a karshe su ka kare musu kallon sirri a ranar wani biki na al'ada da Kwairanga ke gudanarwa duk shekara a ka turo maza mayaka daga Damanga, ' yanmata sukashayar da sarakai giyasu bayan sun sha sun bugu su ka hadu su ka cinyesu da yaki da rana tsaka, su ka karkashe mutane su ka nufi fada wajen Sarki, in da ya nuna jarumtarsa a shafi na 9 ' Maharan Damanga su ka yi ca kan Sarki Haruna, shi kuwa gogan naka ko in kula sai faman kirari ya ke yana cewa "Sai ni dan mutan Kwairanga kadangaren bakin tulu, a kar ka a kar tulu a bar ka ka bata ruwa, ruwan dare dama duniya na kwairanga sai dubu ta taru, ai kuwa nan da nan suka taru a kansa su ka kame Sarki Haruna Kabir su ka tafi da shi garinsu su ka daure, cikin matansa kuwa akwai wata da a ke kira Hassana wacce ta haye doki ta kubuta ta gudu tare da goyon danta Usman, 'yar Wani sarki sadauki jarumin gaske ne a wata kasa da a ke kira Yammaniya. Bayan ta sanar da mahaifinta yadda a ka tarwatsa kasar maigidanta Sarki Haruna, sai ya jajanta lamarin kuma ya dauki aniyar horar da Usmanu don ya daukarwa mahaifinsa fansar abinda a ka yi masa.
Sarki Haruna kuwa ya na daure a can wani kurkukun karkashin kasa a kasar Damanga in da ya shafe shekaru cikin wahala da azabtarwa iri-iri, yayin da kuma Zubaida daya daga cikin matan da a ka tura Kwairanga su ka yaudarar da sarakai ta kamu da ciwon son sa ta dinga zuwa har cikin firsuna ta na taimakonsa tare da shan alwashin sai ta fitar da shi daga halin kuncin da ya ke ciki.
Usman na da shekaru bakwai a ka fara shigar da shi daji a na gogar da shi ilimin yaki tun daga kan fada da mutane har zuwa dabbobi tare da koya masa dabarun fada da takobi da mashi da iya harbi da kwari da baka da sauransu.
Ya na da shekaru goma sha biyu ya kware sosai ya zama sadauki a fagen yaki duk kasar yammawa an sallama masa har su na yi masa kirari a shafi na 12 su na cewa " Usman Mai duniya na Kaura yalli, gwaggon biri makashin maza".
A lokacin ne a ka sanar da Usman labarin mahaifinsa da irin wulakancin da Damangawa su ka yiwa masarautarsa.
Ai kuwa Usman Mai duniya ya shirya tare da abokinsa Sabi'u wanda su ka taso tare dan Kaura yalli wato kawun Usmankenan, su ka nausa daji.
Shi kuwa Sarki Haruna Kabir Zubaida ta kubutar da shi daga gidan kurkukun sun shiga duniya, in da suka yi aure daga bisani wahalar da ya sha a kurkuku ta kwantar da shi ciwo.
Jarumta
Usman kuwa tun shigarsu daji ya ke nuna jarumtarsa in da ya kashe Gada suka cinye a shafi na 23, sannan ya gwabza yaki da wasu 'yan rawar wuta a shafi na 26, ya yi gumurzu da Sarkin fawa a shafi na 27. Sun buga gumurzu da mayakan garin Dawaki a shafi na 32 in da su ka biyo bayansu, maimakon Usman ya gudu sai su ka tsaya suna cafe mashi da kibbau, in da ya ke yi wa kansa kirari, "Kai arna ba ku sanni ba ne? Ni ne Usman Mai duniya, gwaggon biri makashin maza ni ne hadari malfar duniya". Nan ya afka musu ya karkashe su.
Haduwarsu da aljani wanda ya ba Usman takobin kakansa da suka ara su kai yaki a shafi na 33-34.
Usman ya shiga gasa a kasar Zainawa in da ya yi dauki ba dadi da mayaka abokan takara a shafi na 36.
Sannan ya gwabza da sarkin yakin garin Kaura Malle wanda manyan baraden nahiyar ke shakkar arangama da shi saboda rashin tausayinsa, amma Usman bai saurara ba sai da ya fatattaka jikin Kaura Malle ya cinye gasar a shafi na 37-39.
Ya taimakawa Sarkin Zainawa sun yaki mutanen kasar Dawaki in da ya gwabza da manyan mazaje da kauraye a shafi na 55 sannan ya yi gumurzu da Sarkin in da ya shafe shi a doron kasa........
Za mu ci gaba a sati mai zuwa.....