Tuesday, 7 January 2020
Murucin Kan Dutse...
(Tsakure daga wani sashe na sabon littafina)
Babi Na Bakwai
Babu kakkautawa ruwan bamabamai ake daga sojojin ruwa na Najeriya, wanda cikin kwana uku babu sararawa. Wai da an ji shiru, an dauka bako ya tafi ko kuma makamansa sun kare, sai a ka ji sabon hari. Ashe wannan wani salon yaki ne na sojojin Najeriya, wannan salon nasu ya sha banban da abin da suke zaton abokan hamayyarsu zasu zata.
Da farko dai sun san cewa manyan sojojin Biyafara suna gaba da mafi yawan sojojinsu, bayan wannan sun halarci makarantu na horon sojoji a Birtaniya da Amurka da Indiya zuwa Ghana tare. Don haka suna kyautata zato duk wani motsi da suka yi, watakila wannan yayyen nasu dake cikin Biyafara su fahimta. Hakan yasa dole su yi takatsantsan.
Ga yadda abubuwa suke tafiya kamar an yi yamma da kare ne, domin yayyen nasu sun gaza fahimtarsu a wannan lokaci. Wannan luguden wuta da ake ashe ana so a bawa rundunar Isaac dama ne ta isa James Town. Shi ma Akininde dake tsaunin Bonny zai yunkuro da tashi rundunar ya kawo wa Isaac dauki. Haduwarsu zai taimaka a kama James Town cikin sauki. Hakan kuwa aka yi, cikin kankanin lokaci rundunar ta 3MCDO ta danna da qarfin tsiya ta mamaye wannan gari.
Wai duk wannan dawurwura da ake ashe dai ba ita ba ce ainahin abin da ake son cimmawa, duk dai salon yaudara ne na yaki. Wannan dabara kuwa ta kara tabbatarwa sojojin Biyafara cewa lalle sojojin kasar Najeriya na kokarin cin Fatakwal ne daga Tsaunin Bonny, domin dai ga su sun danno har sun shigo James Town.
Hakan yasa suka sakankance suka firfito daga maboyarsu, musammam irin gwalalo da a kan gina saboda buya ga harsasai da ruwan bama-bamai. Cikin wannan dauki babu dadin da ake ta yi, wannan bataliya ta Najeriya ta dauke hankalinsu ga sharrin da ake kulla musu. An ce dama yaki dan zanba ne, wannan duk wata dabara ce da zata bawa ainahin sojojin Najeriyar dake tafe cikin surkikiyar daji su 35, 000 su samu damar isowa garin Oron, wanda daga nan ne zasu gangara zuwa kogin Opobo.
Amma fa dole su zamo a shirye, kuma su kula. Domin yayin da suka ba wa kogin Opobo baya, sojojin na Biyafara za su so su tarfa su, yadda idan wuta ta yi wuta su yi kokarin dannasu har sai sun dangane da ruwan dake bayansu. Watakila za su so yin abin da suka yi wa runduna ta biyu ta Najeriya, wanda suka yi kokarin sulalowa ta cikin kogin Naija a kokarinsu na shiga Asaba. Runduna ta biyu ta samu nasarar haurowa da wasu daga cikin makamansu, amma yayin da sojojin na ‘yan tawaye suka tarfa su sun kasa kare kansu, wanda da yawansu sun mutu ko dai da harsashi ko kuma sun nutse a ruwa.
Sojojin na Najeriya na samun karfin gwiwa, musamman yadda abubuwa ke tafiya daidai kamar yadda aka tsara, illa ‘yan kananan matsaloli da sukan yi kokarin magance su. Duk inda suka bullo sukan fito ne ba tare da abokan gaba sun sani ba, don haka cikin ruwan sanyi suke kama su.
Ai kuwa a cikin wannan yanayi na rashin takamaimai me yake faruwa tawagar su Sanusi ta karaso cikin duhun dare ga kuma ruwan sama da ake tafkawa. To amma kuma abin ka da baki da basu san dawan garin ba, maimakon su sauka a Oron kamar yadda aka tsara, sai sojojin suka sauka a Tsaunin Parrot, wanda yake hannun riga da Oron xin. A wannan lokaci sojojin ruwa na Najeriya sun shiga kwana na uku suna sakin wuta, wanda dole a sanar da su cewa sojojin sun iso, amma sun sauka a Tsaunin Parrot kuma ba kamar yadda aka tsara ba. Dole a sanar da su sojojin na yunkurin haurawa su karasa Oron, wanda hakan na nufin sai sojojin ruwan sun tsahirta da sakin wuta su dan sha ruwa. Hakan sai ya bawa su Sanusi damar haurawa suka shiga ainahin inda ake son su sauka.
A lokacin da sojan ruwan suka tsahirta, abin fa bai tsaya haka ba sai sojojin sama suka dauki na su ta wani salo da kwata-kwata hankalin abokan gaban zai karkata daga Oron. Ka san ginshikin sojojin dake tafe za su haura ne ta cikin ruwa, inda za a yi amfani da kwale-kwale. Don haka sai an yi da gaske, kar abokan gaba su far musu a wannan lokaci. Hakan yasa ba a yi sakaci ba, aka ba wa sojojin sama ta su damar.
Sojojin saman sun shiga nasu barin wuta ta bangaren arewa zuwa Uyo da kuma yamma da kogin Opobo. Hakan zai sa runduna guda biyu dake fuskantar abokan gaba ta dauke hankalinsu, su zaci sune ainahin babbar rundunar Najeriya, inda ake kyautata zato za su rike wuta suna mai fuskantar Oron, da kuma gabas da ita ta bangaren wani karamin gari da ake kira Okopedi, su ma su rike wuta.
Innalillahi Wa’inailahir Rajiun, wanda bai san yaki ba shi yake nemansa. Babu abin da kake ji sai qarar manyan-manyan bindigu. Wasu bindigun kana jin kararsu ka san bindugun nan ne da ake kira 2 Inch da kuma 81 mm mortars. Su kuma abokan gaba kasancewar sun san cewa zai yi wuya a shammace su ta baya, saboda yanayin gurin da ba zai ketu ba suka sakankance har ba su girke manyan bindigu kirar 2 inch da 81 mm mortars.
Ana cikin gwabza wannan yaki, kamar daga sama sai sojojin ‘yan tawaye suka ji wani sabon hari da karar bindigu ta inda ba sa zato, su waiwaya haka sai suka ga wata runduna ce mai tarin yawa ta vallo ta bayansu tana tafe kamar bakin gajimare. Lahaula Walaquwata Illabillah, ta ina wadanna sojojin masu tarin yawa suka faso kamar aljannu. Su dai a iya saninsu babu wata hanya takamaimiya saboda ruwa da yanayi na chabi da bishiyoyi na kurmi. Wani gurin ma idan ruwa ya yo ambaliya, ya kan hadiye mutum har wuya, ko kuma irin wannan tabon mai kama da ruwan gam da kan shanye mutum a hankali yana ji yana gani.
Zaharaddeen Ibrahim Kallah
Subscribe to:
Posts (Atom)