Friday, 23 December 2011

RANAR HADUWA


  1. Ya rabbana salli ala,
Muhammadun hairul ambiya.
  1. Nai godiya gun rabbana,
Sarkin da yai yi sammaniya.
  1. Shi ne ya sa so zuciya,
Har ma na so wata Gimbiya.
  1. Cikin dare ko safiya,
Ko ko cikin barci xaya.
  1. Ran haxuwa da sarauniya,
Rana ce ta ruxiya.
  1. Nai sallama qofar gida,
Ta fito kamar Hawainiya.
  1. Haske da qamshi yai gaba,
Fuska tana walainiya.
  1. Murmushinta na da kyau kwarai,
Balle idan ta yi dariya.
  1. Ta nuna so kuma zahiri,
Ta sacen dukkan zuciya.
  1. Hankali gare ta ‘yan uwa,
Ga tawakkali ga masoyiya.
  1. In ko tana zance na ta,
Tamkar a ce ‘yar masaniya.
  1. Tunanin wagga sahiba,
Ya zam kamar zinariya.
  1. Ilmi a gun ta  sarauniya,
Al’amarin ba fariya.
  1. Kyawun diri na masoyiya,
Allahu yai wa Gimbiya.
  1. Tauraruwar  mata  ki ke,
Mai haskake mun zuciya.
  1. Muryarta na jan hankali,
Sanyinn idaniya Gimbiya.
  1. Ranar haxuwa da sahiba,
Ranar an sacen zuciya.
  1. Nai kira ga masoyiya,
Ta xago tana dubanniya.
  1. Murmushinta na jan hankali,
Na zam cikin ruxiya.
  1. Allah shi ya haxa mu a yau,
Ga ni ga ki ya sarauniya.
  1. Yau Magana ce ta gaskiya,
A bisa tafarkin gaskiya.
22. Haqiqa kin narkan zuciya,
                        Gavovi har ma jijiya.
  1. “Dalin” ka sacen zuciya,
Dare da rana bai daya.
  1. Begenka shi ke ja da ni,
Na zam kamar bebanniya.
  1. Amsarta kenan sahiba,
Wadda ke sa ni tunaniya.
  1. Inubi abar tsotsa garen,
Sheqi gareta da walqiya.
  1. Qamshi gareta Gimbiya,
Kamshi kamar na furanniya.
  1. Allahu roqo nai maka,
Ka ba ni sanyin zuciya.
  1. Nai godiya ga ilahina,
Ka sa mu riqe ta gaskiya.
  1. Kare mu shairin maqiya,
Masu son ganin mu tsiya-tsiya.


23 Ga Watan Afirilu, 2003.

© Zaharaddeen Ibrahim Kallah


No comments:

Post a Comment