Friday, 4 September 2015

TARON BIKIN MARUBUTAN HAUSA NA DUNIYA



Wasu daga cikin mahalarta taron

Marubutan Hausa sun xauki xamara don gudanar da bikin marubutan Hausa na duniya. A ranar Asabar ne 6 ga Yuni, 2015 aka gudanar da zama na farko na shire-shiryen gabatar da taron. Tunanin shirya wannan biki ya taso ne bayan tattaunawa tsakanin marubuta ta kafofin intanet, wanda ya biyo kafa kwamitin da zai jagoranci taron karqashin Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON. Ana sa ran taron zai haxo marubuta daga faxin duniya musamman qasashen da suke na Hausawa da makwabtansu. 

A yayin qaddamar da kwamitin, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON, ya yi bayanin amfanin ranar ga marubutan Hausa. A cewarsa taron zai haxa tsofaffi da sababbin marubuta don tattaunawa da musayar ra’ayin a kan cigaban adabin Hausa. A yayin taron ana sa ran za a yi bajakolin littattafai sannan a gabatar qasidu da taron sanin makamar aiki da karance-karance qirqirarrun labarai da waqoqi.

Marubuta daga Kano da Katsina da Kaduna da Jigawa na daga cikin waxanda suka samu damar halarta taron qaddamar da kwamitin da tattaunawa. Hakazalika, qungiyoyin marubuta na daga cikin waxanda za su taka rawa a wajen ganin nasara shirin. Ana sa ran za a yi taron a watan Oktoba na wannan shekara a garin Kano. An zavi Kano ta kasance garin da za a gudanar da taron saboda matsayin jihar wajen raya adabin Hausa, musamman ta vangaren haziqan marubuta da jihar ke da su da kuma rubuce-rubuce da kasuwancin littatafai. 

Akwai fatan cewa bayan an gudanar da taron za a samu cigaba a harkar rubutun Hausa ta yadda za a shigo da sababbin tsare-tsare da zasu inganta harkar. Musamman yadda marubuta ke kuka na lalacewar harka a wannan lokaci. A halin yanzu marubutan Hausa ba kowa ba ne yake iya sayar da koda kofi dubu biyu na litatttafansu duk da xinbin al’aummar da qasar Hausa take da ita. A Kano a shekarun baya, akwai marubutan da sun sayar da kofi sama da dubu xari shida na littafinsu a lokacin da ake ganin Kanon ma ba ta tunbatsa ba. 

An shiga wani qarni da matasa ba sa son karance-karance, duk da cewa wasu na ganin matsalar ba ta rashin karance-karance ba ce. Amma maganar gaskiya matasa a yanzu sun fi mayar da hankalinsu wajen hawa kafofin yanar gizo ko intanet da kallon fina-fina, wanda hakan ya kawo naqasu ga harkar ilimi da adabin ma. Sanin kowa ne babu alummar da zata cigaba matuqar matasan ta basa karatu.
Ina ganin lokaci ya yi da gwabnatin jihar Kano tare da hukomomi na ilimi za su haxa kai don jagorantar farfaxo da harkar rubutu, ta yadda za a qarfafi marubutan mu na gida da su yi rubuce-rubuce masu nagarta, da yin tsare-tsare da zasu inganta harkar. Misali, sanya gasar rubuce-rubuce, xaukar nauyin yin wasu rubuce-rubuce masu fa’ida da tarurrukan qarawa juna sani. 

A wannan duniya da muke ciki ta bani gishiri in ba ka manda, ba abin da ake buqata illa gudunmawar da kowace al’umma za ta iya bayarwa na cikar da duniya gaba. Allah ya taimaki rubutu na marubuta gaba xaya.

Daga,

Zaharaddeen Ibrahim Kallah

Wednesday, 2 September 2015

Ganawar Marubuci Farfesa Yusuf Adamu da Daliban Kwalejin Sa'adatu Rimi

A Ranar Lahadi (12-7-2015), daliban Sashen Hausa na Kwalejin Sa’adatu Rimi suka karbi bakuncin Farfesa Yusuf M. Adamu, tsohon shugaban kungiyar Marubuta ta kasa (ANA) reshe Jihar Kano. Taron ya gudana ne bayan daliban da ke (part time) na kwalejin sun yi nazari a kan littattafin Farfesan mai suna Idan So Cuta Ne, wanda aka rubuta tun a shekara ta 1989.
Farfesa Yusuf Adamu na rubutu cikin harshen Hausa da Turanci, ya fitar da littattafai masu yawa wadanda suka hada da Ummul-Khairi da Maza Gumbar Dutse da Gumakan Zamani. A littattafansa na Turanci akwai Butterfly and Other Poems da Animal in the Neighbourhood da Landscapes of Poetry da They Can Speak English da A flat World da sauransu.
Taron ya kayatar matuka, domin ba ya ga marubucin, wasu daga cikin marubuta sun halarta wadanda suka hada da Zaharaddeen I. Kallah da Dokta Faruk Sarkin Fada da Kabiru Yusuf Anka. Sannan akwai da yawa daga cikin malaman Sashin Hausa na kwalejin, karkashin jagorancin Shugabar Sashin, Dokta Bilkisu Yusuf, wadda Dokta Mahe Isa Ahmed ya wakilta.
A yayin jawabin maraba, Dokta Mukhtar Sadauki ya sanar da cewa wannan rana ita ce rana ta karshe da daliban suka gama daukar darasi a kan wannan fanni, hakan yasa suka gayyaci marubucin littafin da aka nazarta wato Farfesa Yusuf M. Adamu don ya amsa tambayoyi daga daliban.
Farfesa Yusuf Adamu ba boyayye ba ne a bangaren rubuce-rubuce, domin yana daga cikin jiga-jigan da suka haifar da Adabin Hausa na zamani. Tun bayan da kamfanin wallafa littattafai na NNPC ya dakatar da buga littattafan Hausa, marubuta na wannan zamani suka shiga mawuyacin hali na rashin samun kafar da za su isar da sakonninsu. A cikin wannan hali ne marubuta irin su Talatu Wada da Farfesa Yusuf Adamu da Ado Ahmad Gidan Dabino da Sunusi Shehu Daneji da dan’Azimi Baba da su Balaraba Ramat da su Adamu Muhammad da Alkhamees D. Bature da Bala Anas Babinlata da sauransu suka jagoranci nakudar Adabin Hausa na zamani. Hakika zan iya cewa gudunmawarsu ta taka rawa wajen dawwamar da Adabin Hausa har ya zama a raye zuwa wannan lokaci. A yau idan ana maganar marubutan da suke rubutu cikin harshen uwa, yana cikin wadanda suka yi fice. Wannan abin alfahari ne ga duk mai kishin yare da al’ada ta Hausa.
Farfesa Yusuf, yayin gabatar da tarihinsa da tarihin fara rubuce-rubucensa, ya gabatar da yadda ya fara sha’awar sauraron labarai da tatsuniyoyi, wadanda sun taimaka wajen zamansa marubuci. A cewarsa, mahaifinsu kan dauke su lokacin hutu zuwa wasu garuruwa, inda bayan sun dawo yakan ummarce su da su rubuta abin da suka gani. Da haka ya fara rubutu, inda ya rubuta littafinsa na farko Maza Gumbar Dutse, sai kuma Idan So Cuta Ne… da ya rubuta shi a cikin mako guda. A cewarsa, har yakan zana yadda yake son wani abu daga cikin bayaninsa ya kasance ya yi rubutu.
Hakika wannan dan gajeran tarihi zai haska wa wadanda suke da sha’awar zama marubuta da su yi koyi da shi, su fahimci suna da baiwar rubutu. Na san da yawa daga cikin mutane suna da wannan baiwa amma ba su sani ba. Misali, akwai mutane da idan suna ba ka labari sai ka rantse suna nan aka yi abu, ko kuma ka ga wadanda ke da sha’awar sauraron tatsuniyoyi da labarai, babu shakka hakan na nuna cewa za su iya zama kwararrun marubuta.
Kamar yadda na ce a baya, taron ganawa da daliban ya yi armashi kwarai, domin ya ba su dama sun yi tambayoyi ga Farfesa sannan sun gana da wasu daga cikin marubutan Hausa. Hakan ya sa an yi musayar ra’ayi da fito da wasu muhimman bayanai a kan adabi. Daga cikin abubuwan da aka duba sun hada da alakar marubuci da labarin da ya rubuta. Wasu daga cikin mahalarta taron sun yi duba ga wannan bangare. Misali, marubucin Idan So Cuta Ne… dan boko ne wanda ya kai matsayin Farfesa, hakan ya yi tasiri a cikin littafinsa na amfani da ’yan boko a cikin taurarin labarinsa. Kusan kowa yana yin boko, illa wasu kalilan da ba ’yan boko ba wadanda su ma sun taka rawa wajen fito da jigon labarin.
An kawo misalai na Abdulmalik da Salisu da Zairo a wasu daga cikin ’yan book, sai kuma Hajiya Bilkisu a matsayin wadda ba ta yi boko ba, kuma hakan ya kawo matsala ga Abdulmalik da Farida a kan soyayyarsu.
Daga cikin abubuwan da daliban suka tambaya, har da abin da ya ja hankalin marubucin ya yi wannan littafin. Yayin ba da amsa, marubucin ya ce ya jima yana jin ana maganar duk wata soyayya da aka jima ana yi a karshe zai yi wuya a yi aure. Kasancewar yana da wacce yake so kuma sun jima tare sai ya fara tunanin abin da zai faru idan haka ta faru, wannan ne ya sa ya fara tunanin yadda zai ba kansa hakuri. Wannan ne ya sa ya rubuta littafin Idan So Cuta Ne…
daliban sun yaba wa marubucin a kan cewa an rubuta littafin tun 1989 amma sai a dauka a wannan lokaci aka rubuta shi. An kuma yaba masa yadda littafin ya kasance tsaftatacce da al’umma za su amfana da shi.
Sauran baki su ma sun tofa albarkacin bakinsu a kan taron. A nasa bangaren, Zaharaddeen Kallah ya nuna farin cikin kasancewa a wurin taron, musamman saboda sha’awa da daliban suka nuna na nazarin Adabin Hausa. Ya kuma ba su shawara da su yi alfahari da harshen Hausa wanda a halin yanzu ya dauki hanyar shahara sosai a fadin duniya. Ya nemi daliban su kasance masu dabi’ar karance-karance da nazarin littattafai, wanda hakan zai taimaka musu matuka, musamman ga wadanda ke da sha’awar zama marubuta.
Dokta Faruk Sarkin Fada kuma ya yaba wa Sashen Hausa na kwalejin saboda wannan abu da suka shirya wanda zai taimaka wa daliban a cikin karatunsu. Ya yi kokarin fahimtar da daliban tasirin rubutu, musamman da aka samu wata daga cikin daliban marubuciya ce. A cewarsa yana da kyau mutum ya yi rubutu ba kawai don abin da zai samu ba, sai don manufarsa a rubutu wanda ilmantarwa da gyara al’umma ke ciki. Ya ce da yawa daga cikin marubuta sai sun bar duniya sannan rubutunsu ke shahara. Ya ba da misali da Muhammad Ikbal daga tsohuwar kasar Indiya da Pakistan wanda rubutunsa ya yi tasiri wajen kawo juyin juya hali a kasar Iran, bayan tsawon lokaci da rasuwarsa. Duk da cewa Ikbal bai taba zuwa Iran ba, rubutunsa da aka fassara ya yi tasiri sosai a can. Wannan ya sa a yanzu har maulidinsa suke gudanarwa saboda jin dadin abin da rubutunsa ya yi. Daga karshe sai Dokta Faruk ya ba da gudunmowar littattafansa guda uku da ya buga da Hausa ga Sashen Hausa na kwalejin.
Taron ya zo karshe da jawabin godiya daga bakin Dokta Mahe Isa Ahmed, wanda ya gode wa Farfesa Yusuf Adamu saboda lokacinsa da ya ba da na amsa gayyatarsu. Ya kuma gode wa sauran marubuta da suka halarci taron, a inda ya nuna aniyar sashen na kulla alaka da kungiyar Marubuta ta Najeriya (ANA) reshen Jihar Kano don ciyar da adabi gaba.
Hakika wannan alaka da kwalejin marubuta za su yi farin ciki da ita, musamman don za ta kasance hanya da za a taimaki juna. A bangaren dalibai zai kasance hanyar nazari da horar da su a harkar nazari tare da ganawa da marubuta. A bangaren marubuta da suke bukatar manazarta don rubutunsu ya ci gaba da rayuwa, su ma abin alfahari ne. Tabbas wannan yunkuri abin maraba ne musamman a wannan lokaci da ake neman yin wancakali da koyar da harshen Hausa a makaratun sakandire na kasar nan, wanda haka kan iya kawo barazana ga harshen gaba daya.
Zaharaddeen Ibrahim Kallah, tsohon sakataren kungiyar Marubutan ta Najeriya ne reshen jihar Kano, sannan ma’aikaci a Jami’ar Bayero, Kano. dinik2003@yahoo.co.uk

Friday, 16 January 2015

YADDA ZAHARADDEEN YA ZAMA SADAUKI MAI DUNIYA II

Ci gaba daga makon jiya
Yadda Zaharaddeen ya zama Sadauki Mai Duniya.

Matan nan su kai nasarar mamaye gidajen sarakan Kwairanga in da a karshe su ka kare musu kallon sirri a ranar wani biki na al'ada da Kwairanga ke gudanarwa duk shekara a ka turo maza mayaka daga Damanga, ' yanmata sukashayar da sarakai giyasu bayan sun sha sun bugu su ka hadu su ka cinyesu da yaki da rana tsaka, su ka karkashe mutane su ka nufi fada wajen Sarki, in da ya nuna jarumtarsa a shafi na 9 ' Maharan Damanga su ka yi ca kan Sarki Haruna, shi kuwa gogan naka ko in kula sai faman kirari ya ke yana cewa "Sai ni dan mutan Kwairanga kadangaren bakin tulu, a kar ka a kar tulu a bar ka ka bata ruwa, ruwan dare dama duniya na kwairanga sai dubu ta taru, ai kuwa nan da nan suka taru a kansa su ka kame Sarki Haruna Kabir su ka tafi da shi garinsu su ka daure, cikin matansa kuwa akwai wata da a ke kira Hassana wacce ta haye doki ta kubuta ta gudu tare da goyon danta Usman, 'yar Wani sarki sadauki jarumin gaske ne a wata kasa da a ke kira Yammaniya. Bayan ta sanar da mahaifinta yadda a ka tarwatsa kasar maigidanta Sarki Haruna, sai ya jajanta lamarin kuma ya dauki aniyar horar da Usmanu don ya daukarwa mahaifinsa fansar abinda a ka yi masa.
Sarki Haruna kuwa ya na daure a can wani kurkukun karkashin kasa a kasar Damanga in da ya shafe shekaru cikin wahala da azabtarwa iri-iri, yayin da kuma Zubaida daya daga cikin matan da a ka tura Kwairanga su ka yaudarar da sarakai ta kamu da ciwon son sa ta dinga zuwa har cikin firsuna ta na taimakonsa tare da shan alwashin sai ta fitar da shi daga halin kuncin da ya ke ciki.
Usman na da shekaru bakwai a ka fara shigar da shi daji a na gogar da shi ilimin yaki tun daga kan fada da mutane har zuwa dabbobi tare da koya masa dabarun fada da takobi da mashi da iya harbi da kwari da baka da sauransu.
Ya na da shekaru goma sha biyu ya kware sosai ya zama sadauki a fagen yaki duk kasar yammawa an sallama masa har su na yi masa kirari a shafi na 12 su na cewa " Usman Mai duniya na Kaura yalli, gwaggon biri makashin maza".
A lokacin ne a ka sanar da Usman labarin mahaifinsa da irin wulakancin da Damangawa su ka yiwa masarautarsa.
Ai kuwa Usman Mai duniya ya shirya tare da abokinsa Sabi'u wanda su ka taso tare dan Kaura yalli wato kawun Usmankenan, su ka nausa daji.
Shi kuwa Sarki Haruna Kabir Zubaida ta kubutar da shi daga gidan kurkukun sun shiga duniya, in da suka yi aure daga bisani wahalar da ya sha a kurkuku ta kwantar da shi ciwo.
Jarumta
Usman kuwa tun shigarsu daji ya ke nuna jarumtarsa in da ya kashe Gada suka cinye a shafi na 23, sannan ya gwabza yaki da wasu 'yan rawar wuta a shafi na 26, ya yi gumurzu da Sarkin fawa a shafi na 27. Sun buga gumurzu da mayakan garin Dawaki a shafi na 32 in da su ka biyo bayansu, maimakon Usman ya gudu sai su ka tsaya suna cafe mashi da kibbau, in da ya ke yi wa kansa kirari, "Kai arna ba ku sanni ba ne? Ni ne Usman Mai duniya, gwaggon biri makashin maza ni ne hadari malfar duniya". Nan ya afka musu ya karkashe su.
Haduwarsu da aljani wanda ya ba Usman takobin kakansa da suka ara su kai yaki a shafi na 33-34.
Usman ya shiga gasa a kasar Zainawa in da ya yi dauki ba dadi da mayaka abokan takara a shafi na 36.
Sannan ya gwabza da sarkin yakin garin Kaura Malle wanda manyan baraden nahiyar ke shakkar arangama da shi saboda rashin tausayinsa, amma Usman bai saurara ba sai da ya fatattaka jikin Kaura Malle ya cinye gasar a shafi na 37-39.
Ya taimakawa Sarkin Zainawa sun yaki mutanen kasar Dawaki in da ya gwabza da manyan mazaje da kauraye a shafi na 55 sannan ya yi gumurzu da Sarkin Dawakin in da ya gwada masa cewa jarumta fa ba a karami take ba kuma ba a babba ta ke ba, a wajen mai zuciya ta ke.
Usman da Sabi'u sun gwabza gumurzun yaki da mayakan kasar Damanga a Kasar Dadin kowa a shafi na 88/90.
Sun sake kutsawa yaki kasar Kwairanga daukar fansa domin bayan ture Sarki Haruna Kabir sai Sarki Sakimu ya dora kaninsa Mantau a gadon sarautar kasar, a shafi na 101/103, su Usman Mai duniya da Sabi'u sun kawar da Sarki Mantau yayin da Sarki Haruna ya koma kan gadon Sarautarsa da Damagawa su ka tsige shi.
Jarumtar kwarai mai nuna bajinta da ban sha'awa ta mayakan hadin gwiwan kasar Dadin kowa da Zainawa da Kwairanga da kuma Kaura Yalli na kasar yammaniya ta yi arangama da rundunar mayakan Kasar Damanga domin daukar fansa a kan Sarki Sakimu wanda ya addabi yankin a shafi na 105/110 wannan gumurzu shi ne ma fi hatsarin gaske da sarakunan su ka yi. Mata ma ayarin gimbiya Sailuba sun buga gumurzu karkashin Batulu in da su ka karkashe mazajen Damanga.
Usman ya yi arangama da Sarki Sakimu in da su ka yi ta dauki ba dadi ga juna har dai Usman ya sassare masa hannuwa biyu tun daga kafada duk da ganin an kassara Sakimu Zakin Hamada mayakansa ba su saduda sun gwada tsabar taurin kai da masifa sai da Usman mai duniya ya shayar da su ruwan kokon mutuwa, jini ya dinga kwarara, hannuwa da kafafuwa iri-iri kawuna kuwa ba adadi sannan 'yan tsirarun Damangawa su ka sallama, a ka ja Sarki Sakimu zuwa kasarsa ta Damanga gaban talakawansa da ya ke yiwa zalunci ya ke kashewa da izza a ka kashe shi, a ka ba talakawa zabi su ka zabo wanda su ke so a ka nada musu.
Soyayya,
Sarki Haruna ya yi soyayya da Zubaida a shafi na11/12, 21/24 wacce soyayya ce mai cike da tausayi tare da nunawa juna kauna In da a karshe su ka yi aure.
Usman mai duniya da Gimbiya Sailuba 'yar sarkin Zainawa a shafi na 40/42, 47/48
Soyayya ce ta sadaukarwa da nuna tarairayar juna.
Sabi'u ya yi soyayya ta hakika da Safara'u 'yar hakimin Dawaki a shafi na 27/29 in da ya yi takara da dan Galadiman garin.
Usman ya yi soyayya da Aisha a kasar Dawaki.
Littafin ya cika burin taurarin na daukar fansa tare da kai su karagar sarauta da kuma auren matayen da su ke so.
Bugu
Babu laifi a bisa bugun littafin da kuma wallafuwarsa a dunkulallen littafi guda daya da kasantuwarsa mai sahihiyar lambar bugu ISBN.
Tsarin shafuka ya tsaru.
Zanen bango ya dakko hoton ainahin gumurzun da ke cikin labarin.
Kura-kurai
An ce komin iyawarka da kallo mai kallon ka ya fi ganinka, duk irin kokarin da a ka yi wajen kiyaye dokoki da ka'idodin rubutu an dan samu hadewar wasu kalmomi da ya dace a rarrabasu a shafi na 4 koina maimakon ko'ina
a shafi na 5 suka maimakon su ka.
Irin wadannan kananan kura- kurai dai a kan same su tsilla-tsilla cikin littafin.

YADDA ZAHARADDEEN YA ZAMA SADAUKI MAI DUNIYA

Daga Sa'adatu Baba Ahmad Leadership Hausa
31/01/2014

Hira da Marubuci Zaharaddeen Ibrahim Kallah tare da Sharhin Littafinsa Sadauki Mai Duniya....
Ya ya sunanka?
Suna na Zaharaddeen Ibrahim Kallah
Kadan daga cikin tarihin ka?
An haife ni a unguwar Fagge da ke Kano, na yi makarantar firamare na a makarantar firamare ta Giginyu wanda daga nan kuma na koma firamare ta Race Course da ke filin sukuwa a Kano. Bayan nan na wuce makarantar sakandire ta Stadium don yin karatuna na gaba da firamare. Da na qare ne sai na je kwalegin share fagen shiga jami’a ta CAS, Kano. Daga nan ne na samu shiga jami’ar Bayero da ke Kano in da na yi digiri na karanci abin da ya shafi ilimin zamantakewar xan adam tare da siyasa (Sociology/Political Science). Na yi hidimar qasa ta a jihar Kwara wanda na koyar a wata sakandire da ke Patigi. Bayan nan na fara aiki da NGO na wani lokaci kafin na koma Jami’ar Bayero da aiki. A Bayero na koma na yi digiri na biyu a vangaren karatun ci gaban duniya wato (Development Studies).
Wacce shekara ka fara rubutu?
Na fara rubutu a shekara ta 1995 bayan na qare sakandire, xan zaman da na yi kafin na cigaba da makaranta na ga ya dace na fara rubutu.
Wacce shekara ka fara wallafa littafi?
Kafin fara buga littafi na rubutu na ya fito ne a littattafai na gamayya na turanci a wajen 2002, littafin Hausa kuma sai a 2006 littafina “Ciki Da Gaskiya” da muka yi qarqashin hukumar A Daidaita Sahu ya fito.
A matsayinka na marubucin Hausa da turanci, wanne rubutune ya fi ma sauki da ba ka sha'awa a cikinsu?
A matsayina na Bahaushe babu rubutun da ya fi mun sauqi kamar rubutu da Hausa, a cikinsa ne na fara rubutu da kuma shi ne na buxi ido. Tun a firamare a lokacin ina Monita na kan karantawa ‘yan ajina Littattafai irinsu “Ilya Xan Mai Qarfi”da “Magana Jari Ce”.
Zuwa yanzu me ka fahimta game da salo da harshe?
Salo na nufin tsari na rubutu da marubuci ya yi amfani da shi wajen isar da saqonsa. Salon da ake amfani da shi ya danganta da marubuci, wani kan yi amfani da salo mai sa karsashi da jan hankali, wani kuma kan yi amfani da salo mai wahalar da mai karatunsa.
Harshe hanya ce ta isar da saqonni, wanda ta qunshi kalmomi da suke bada ma’ana. Marubuci na amfani da harshe don isar da saqonsa ga jama’a wanda ya qunshi tunani da falsafa.
Wadanne marubuta ne gwanayenka a marubutan Hausa?
A vangaren rubutun Hausa ina da gwanaye kamar su Bala Anas Babinlata da Nazir Adam Saleh da Ibrahim Sheme da Bature Gagare da Yusuf M. Adamu
A marubutan turanci fa?
A Turanci akwai Sidney Sheldon da Abubakar Gimba da James Hadley.
Littafinka Sadauki Mai Duniya ya bambamta da littattafan wannan zamanin, menene sirrin?
Littafin Sadauki Mai Duniya labari ne da ya waiwayi shekaru sama da xari biyu baya a lokacin da ake yaqe-yaqe a qasar Hausa. Kafin na fitar da littafin sai da na nazarci salo daban-daban musamman littattafai tsofaffi da suka kawo tarihi da adabi na shekaru aru-aru. Da wannan ne na yi qoqarin fitar da littafin Sadauki Mai Duniya.
Wacce kungiya ka ke ciki?
Ina cikin Qungiyar Marubuta ta Najeriya (ANA) reshen jihar Kano, a halin yanzu ni ne Magatakardarta. Sannan ina cikin wasu qungiyoyi da dama waxanda ba na marubuta ba, waxanda suka haxa da na cigaban alumma.
Sharhin Littafin Sadauki mai duniya....
Sadauki mai Duniya Littafin da ya kere sa'a.
marubuci Zaharaddeen Ibrahim Kalla.
Shekarar bugu-2010
Jigon labari- Jarumta
Yawan shafuka- 150
Bugawa da yadawa- madaba'ar iya ruwa Zaria Road, Kano Nigeria.
ISBN- 987-987-087-880-3
Rabona da karanta wani labari na jarumta wanda har na ke ganin jarumtakar ta kai Sadaukantaka tun wani Fim da na gani na shekaru dari uku na Sarki Liyonaidas na kasar Sparta wanda ya fuskanci barazanar murkushewa idan har k'asarsa ba ta yi mubaya'a ba ga Sarkin Zaksia ba Azskiz wanda azzalumin shugaba ne da babu Sarki mai karfinsa a duk duniya a kuma zamaninsa. Sun yi jayayya da Liyonaidas in da ya gaza zubda Liyonaidas wajen kare martaba da 'yancin k'asarsa. Sun gwabza yaki ga juna amma jarumta ta hana Liyonaidas ya yi hakuri ya janye duk da kuwa Sarki Azskiz ya fi shi karfi tare da jama'a. A karshe dai an kashe Sarki Liyonaidas da dubban masu da kibbau amma wajibi ne a jinjinawa jarumtarsa da gwarzantakarsa.
A lokacin da na ke karatun littafin Sadauki mai duniya na yi ta kamanta jarumtar Usman mai duniya da Sarki Liyonaidas yadda a 'yan shekarunsa na kuruciya ya shiga daji ya kashe Karen ruwa shi ma Usman mai duniya 'yan shekarunsa na kuruciya ya shiga daji ya kashe Goggon biri.
Sadauki Mai Duniya
Wannan littafi ya kunshi labarin wasu masarautu guda biyu masarautar Kwairanga wacce ke karkakashin mulkin sarki Haruna wanda ke gudanar da mulkinsa cikin jarumta da adalci da tausayin talakawa. Yayin da daya masarautar Damanga wacce Sarki Sakimu ya ke gudanar da mulkinta cike da zalunci da izza, ya maida rayukan talakawansa tamkar na fari saboda kisan kai da mugunta, sannan duk wani mikirci tare da kulla salon dabarun yaki ya iya, Sarki Sakimu na da dabi'ar bakin ciki a duk lokacin da ya ji labarin kasar da arzikinta ya kafu ko kasar da ta shahara a fagen yaki ya kan so ya yaketa ta dawo karkashin mulkinsa ko ta wacce hanya ne.
Lokacin da Sarki Sakimu ya ji labarin masarautar Kwairanga ya yi tunani ya ga ba zai iya yakarta ba sai ya shirya makirci ya tura wasu kyawawan mata wadanda kyaunsu ya kai kyau su ka je fada a zuwan 'yan gudun hijirar yaki wanda su ka ce Damangawa sun kashe iyayensu da mazajensu, a taimake su da wurin zama. Sarki Haruna Kabir dai zuciyarsa ba ta kwanta da lamarin ba saboda ya gansu tsaf-tsaf ba wahala ko gajiyar tafiya a tattare da su amma 'yan majalisarsa su ka nuna ba wani abu. Matan nan su kai nasarar mamaye gidajen sarakan Kwairanga in da a karshe su ka kare musu kallon sirri a ranar wani biki na al'ada da Kwairanga ke gudanarwa duk shekara a ka turo maza mayaka daga Damanga, ' yanmata sukashayar da sarakai giyasu bayan sun sha sun bugu su ka hadu su ka cinyesu da yaki da rana tsaka, su ka karkashe mutane su ka nufi fada wajen Sarki, in da ya nuna jarumtarsa a shafi na 9 ' Maharan Damanga su ka yi ca kan Sarki Haruna, shi kuwa gogan naka ko in kula sai faman kirari ya ke yana cewa "Sai ni dan mutan Kwairanga kadangaren bakin tulu, a kar ka a kar tulu a bar ka ka bata ruwa, ruwan dare dama duniya na kwairanga sai dubu ta taru, ai kuwa nan da nan suka taru a kansa su ka kame Sarki Haruna Kabir su ka tafi da shi garinsu su ka daure, cikin matansa kuwa akwai wata da a ke kira Hassana wacce ta haye doki ta kubuta ta gudu tare da goyon danta Usman, 'yar Wani sarki sadauki jarumin gaske ne a wata kasa da a ke kira Yammaniya. Bayan ta sanar da mahaifinta yadda a ka tarwatsa kasar maigidanta Sarki Haruna, sai ya jajanta lamarin kuma ya dauki aniyar horar da Usmanu don ya daukarwa mahaifinsa fansar abinda a ka yi masa.
Sarki Haruna kuwa ya na daure a can wani kurkukun karkashin kasa a kasar Damanga in da ya shafe shekaru cikin wahala da azabtarwa iri-iri, yayin da kuma Zubaida daya daga cikin matan da a ka tura Kwairanga su ka yaudarar da sarakai ta kamu da ciwon son sa ta dinga zuwa har cikin firsuna ta na taimakonsa tare da shan alwashin sai ta fitar da shi daga halin kuncin da ya ke ciki.
Usman na da shekaru bakwai a ka fara shigar da shi daji a na gogar da shi ilimin yaki tun daga kan fada da mutane har zuwa dabbobi tare da koya masa dabarun fada da takobi da mashi da iya harbi da kwari da baka da sauransu.
Ya na da shekaru goma sha biyu ya kware sosai ya zama sadauki a fagen yaki duk kasar yammawa an sallama masa har su na yi masa kirari a shafi na 12 su na cewa " Usman Mai duniya na Kaura yalli, gwaggon biri makashin maza".
A lokacin ne a ka sanar da Usman labarin mahaifinsa da irin wulakancin da Damangawa su ka yiwa masarautarsa.
Ai kuwa Usman Mai duniya ya shirya tare da abokinsa Sabi'u wanda su ka taso tare dan Kaura yalli wato kawun Usmankenan, su ka nausa daji.
Shi kuwa Sarki Haruna Kabir Zubaida ta kubutar da shi daga gidan kurkukun sun shiga duniya, in da suka yi aure daga bisani wahalar da ya sha a kurkuku ta kwantar da shi ciwo.
Jarumta
Usman kuwa tun shigarsu daji ya ke nuna jarumtarsa in da ya kashe Gada suka cinye a shafi na 23, sannan ya gwabza yaki da wasu 'yan rawar wuta a shafi na 26, ya yi gumurzu da Sarkin fawa a shafi na 27. Sun buga gumurzu da mayakan garin Dawaki a shafi na 32 in da su ka biyo bayansu, maimakon Usman ya gudu sai su ka tsaya suna cafe mashi da kibbau, in da ya ke yi wa kansa kirari, "Kai arna ba ku sanni ba ne? Ni ne Usman Mai duniya, gwaggon biri makashin maza ni ne hadari malfar duniya". Nan ya afka musu ya karkashe su.
Haduwarsu da aljani wanda ya ba Usman takobin kakansa da suka ara su kai yaki a shafi na 33-34.
Usman ya shiga gasa a kasar Zainawa in da ya yi dauki ba dadi da mayaka abokan takara a shafi na 36.
Sannan ya gwabza da sarkin yakin garin Kaura Malle wanda manyan baraden nahiyar ke shakkar arangama da shi saboda rashin tausayinsa, amma Usman bai saurara ba sai da ya fatattaka jikin Kaura Malle ya cinye gasar a shafi na 37-39.
Ya taimakawa Sarkin Zainawa sun yaki mutanen kasar Dawaki in da ya gwabza da manyan mazaje da kauraye a shafi na 55 sannan ya yi gumurzu da Sarkin in da ya shafe shi a doron kasa........
Za mu ci gaba a sati mai zuwa.....