Friday, 4 September 2015

TARON BIKIN MARUBUTAN HAUSA NA DUNIYA



Wasu daga cikin mahalarta taron

Marubutan Hausa sun xauki xamara don gudanar da bikin marubutan Hausa na duniya. A ranar Asabar ne 6 ga Yuni, 2015 aka gudanar da zama na farko na shire-shiryen gabatar da taron. Tunanin shirya wannan biki ya taso ne bayan tattaunawa tsakanin marubuta ta kafofin intanet, wanda ya biyo kafa kwamitin da zai jagoranci taron karqashin Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON. Ana sa ran taron zai haxo marubuta daga faxin duniya musamman qasashen da suke na Hausawa da makwabtansu. 

A yayin qaddamar da kwamitin, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino, MON, ya yi bayanin amfanin ranar ga marubutan Hausa. A cewarsa taron zai haxa tsofaffi da sababbin marubuta don tattaunawa da musayar ra’ayin a kan cigaban adabin Hausa. A yayin taron ana sa ran za a yi bajakolin littattafai sannan a gabatar qasidu da taron sanin makamar aiki da karance-karance qirqirarrun labarai da waqoqi.

Marubuta daga Kano da Katsina da Kaduna da Jigawa na daga cikin waxanda suka samu damar halarta taron qaddamar da kwamitin da tattaunawa. Hakazalika, qungiyoyin marubuta na daga cikin waxanda za su taka rawa a wajen ganin nasara shirin. Ana sa ran za a yi taron a watan Oktoba na wannan shekara a garin Kano. An zavi Kano ta kasance garin da za a gudanar da taron saboda matsayin jihar wajen raya adabin Hausa, musamman ta vangaren haziqan marubuta da jihar ke da su da kuma rubuce-rubuce da kasuwancin littatafai. 

Akwai fatan cewa bayan an gudanar da taron za a samu cigaba a harkar rubutun Hausa ta yadda za a shigo da sababbin tsare-tsare da zasu inganta harkar. Musamman yadda marubuta ke kuka na lalacewar harka a wannan lokaci. A halin yanzu marubutan Hausa ba kowa ba ne yake iya sayar da koda kofi dubu biyu na litatttafansu duk da xinbin al’aummar da qasar Hausa take da ita. A Kano a shekarun baya, akwai marubutan da sun sayar da kofi sama da dubu xari shida na littafinsu a lokacin da ake ganin Kanon ma ba ta tunbatsa ba. 

An shiga wani qarni da matasa ba sa son karance-karance, duk da cewa wasu na ganin matsalar ba ta rashin karance-karance ba ce. Amma maganar gaskiya matasa a yanzu sun fi mayar da hankalinsu wajen hawa kafofin yanar gizo ko intanet da kallon fina-fina, wanda hakan ya kawo naqasu ga harkar ilimi da adabin ma. Sanin kowa ne babu alummar da zata cigaba matuqar matasan ta basa karatu.
Ina ganin lokaci ya yi da gwabnatin jihar Kano tare da hukomomi na ilimi za su haxa kai don jagorantar farfaxo da harkar rubutu, ta yadda za a qarfafi marubutan mu na gida da su yi rubuce-rubuce masu nagarta, da yin tsare-tsare da zasu inganta harkar. Misali, sanya gasar rubuce-rubuce, xaukar nauyin yin wasu rubuce-rubuce masu fa’ida da tarurrukan qarawa juna sani. 

A wannan duniya da muke ciki ta bani gishiri in ba ka manda, ba abin da ake buqata illa gudunmawar da kowace al’umma za ta iya bayarwa na cikar da duniya gaba. Allah ya taimaki rubutu na marubuta gaba xaya.

Daga,

Zaharaddeen Ibrahim Kallah

No comments:

Post a Comment