Allah ya bamu ikon cin jarabawarsa. Ita rayuwa, gwagwarmaya ce gaba ɗayanta. Lokacin da Abubakar Imam da takwarorinsa suka tafi Birtaniya a jirgin ruwa, sun samu aƙalla wata ɗaya akan ruwa.
Kullum sai dai su ci su sha, sannan su kwanta. Anan ne Abubakar Imam ya fahimci ashe gwagwarmayar rayuwa tana da daɗi. Ba su da matsalar abinci ko.makwanci, amma kuma duk sun takura.
Duk wani hali da za mu shiga yana cikin gwagwarmayar rayuwa. Wani ya zage ka, ko a taka, ko a ja kaima ka ja, duk ba sabon al'amari ba ne.
Mun yi imani za mu cigaba da gwagwarmaya, domin ita ce tushen rayuwa. Haƙika Allah maɗaukakin sarki yana tare da mu, matuƙar ba mu juya masa baya ba.
Zaharaddeen I. Kallah
zikallah@gmail.com
No comments:
Post a Comment