Na je gidan mai don shan mai, sai da aka gama zuba min, in kunna mota sai batir ya ce bai san zance ba. Aka tura gefe, wanda yake bi na a baya ya ce 'Bari a zuba min man in ba ka batir a tashi motar.'
Can wani mai mota 406 da shi ma ya sha mai, na ga ya yi fakin, ban san me yake ba sai ganinsa na yi ya ciro batir ɗin motarsa da sauri ya nufo mota, 'Buɗe gaban motar.' Ya ce.
Bawan Allah nan shi ya sanya batir ɗin, na tashi motar sannan ya mayar da nawa.
Idan ba a Arewa ba ina za a yi maka haka a Najeriya?
A wani zuwa Abuja da muka yi, muna neman wata hanya, muka tsaya muka tambayi wani mai acaba a gefen hanya. Mutumin sai hawa babur ya yi ya ce mu biyo shi, mun yi tafiya ta kai ta mil uku. Da ya nuna mana hanya sai ya ƙara mai, bai tsaya neman wani abu ba.
Amma a wata tafiya da muka yi zuwa wata jiha a kudu, babban titin gwamnatin tarayya ya ragargaje, wani lokcin sai direbobi sun sauka titi tare da ratsewa daji. Amma muna 'yar tafiya, sai ka ga matasa sun tare hanya. Sai an biya za a wuce, wai ba hanyar gwamnatin tarayya ba ce. Duk wani motsinka a irin wannan gurare sai ka biya.
Allah ya ƙarawa Arewa albarka.
Daga
Zaharaddeen Ibrahim Kallah
No comments:
Post a Comment